WASHINGTON, D.C —
Kungiyar Amnesty International ta ce, hukumomi a Iran na ci gaba da “mummunar danniya,” biyo bayan zanga-zangar da aka gudanar a duk fadin kasar wadda ta yi sanadin mutuwar akalla mutane 304.
A wata sanarwar da hukumar ta fitar a yau Litinin, kungiyar mai kare hakkin bil-Adama wacce ke da hedkwata a birnin London, ta ce hukumomin kasar suna “kame irin na mugunta,” inda su ke damke dubban masu zanga-zanga, ‘yan jarida, ‘yan rajin kare hakkin bil adama, da dalibai, da “nufin hana su kalubalantar mulkin kama-karya,” da Iran ke yi.
A tsakiyar watan Nuwamba ne zanga-zangar ta barke, bayan da gwamnati ta yi shelar karin farashin mai a daidai lokacin da ake fama da radadin takunkumin da Amurka ta kakaba wa kasar.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum