Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Ta Neman Wadanda Su Ka Bata A Kogin Kwara


ana fargabar cewa mutane da dama sun mutu a cikin hatsarin kwale-kwalen
ana fargabar cewa mutane da dama sun mutu a cikin hatsarin kwale-kwalen

An tabbatar da mutuwar mutane 70 a kalla a cikin hatsarin kwale-kwalen

Ma'aikatan ceto na ci gaba da neman wasu mutane da dama da suka bata a kogin Kwara bayan kifewar wani babban kwale-kwalen da aka cunkusawa fasinjoji fiye da kima.

Jami'an hukumar ceton gaggawa ta jahar Naija sun fada a jiya asabar cewa an gano gawarwakin mutane da yawa da suka mutu a cikin hatsarin da ya faru tun ranar jumma'a. Wani jami'in hukumar ya ce mutane hamsin ne iyakacin abun da kwale-kwalen zai iya dauka.

Masu gudanar da bincike sun ce a lokacin da hatsarin ya faru kwale-kwalen ya na cike makil da 'yan tireda masu zuwa cin kasuwar mako-mako a garin Malale a daya bangaren kogin.

Kimanin awowi 24 bayan afkuwar hatsarin wakilin Sashen Hausa Murtala Faruk Sanyinna ya samo karin bayani.
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:29 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG