Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Harbe-Harbe Yanzu Haka A Wasu Kauyuka Biyu A Madagali Jihar Adamawa


Gidajen da suka kone bayan hare-haren Boko Haram a bama, Fabrairu 20, 2014.
Gidajen da suka kone bayan hare-haren Boko Haram a bama, Fabrairu 20, 2014.

'Yan bindiga sun kai farmaki kan kauyukan Kirchiga da Shuwa a yankin karamar Hukumar Madagali ta Jihar Adamawa yanzun nan

Ana can ana harbe-harbe yanzun nan a kauyen Shuwa, bayan da aka kai farmaki kan kauyen Kirchiga da farko, dukkansu a yankin karamar hukumar Madagali ta Jihar Adamawa.

Wakilin Muryar Amurka, Ibrahim Abdul'aziz, yace har yanzu jami'an tsaro ba su samu isa wuraren ba, kamar yadda wasu mazauna wannan wuri suke ta fada.

A kasance tare ad DandalinVOA domin jin karain bayani.
XS
SM
MD
LG