Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Iya Bada Kariya a Loakcin Zabe Tunda Anbada a Lokacin Yakin Kanfe


Zabe
Zabe

Bisa cigaba da korafe korafe da mutanen Najeriya keyi dangane da dage zabe. Yau mun samu tattaunawa da shugaban wata kungiyar matasa Komarat Abdulmajid Babangida Sa’ad, wanda yayi muna karin haske dangane da nashi hasashen, da yasa hukumar zabe me zaman kanta ta dage zaben, daga inda aka shiryar dashi.

Yace yana gani wannan bawani abu bane illa dai ita hukumar zaben na kokarin biyan bukatun jam’iyya mai mulki, kuma wannan wata damace da su ‘yan jam’iyya me mulki su samu damar yin magudi. Don haka wannan bai kamata ace ita hukumar na daukar umurnin gwamnati me ci ba sabo da ita hukumace me zamankanta.

Komarate Babangida, dai ya kara da cewar ai da rashin tsaro ne zai sa a dage zabe, to ya akayi shi shugaban kasa yaje wadannan jihohin don yakin neman zabe, kuma jami’an tsaro suka bashi kariya da ta kamata. Ashe Kenan zasu iya ba ma al’umar wannan yanki kariya don a gudanar da zabe yadda yakamata. Yana dai ganin wannan bai yi daidai da tsarin demokaradiyya ba.

Ya kara da cewar yakamata kasashen duniya suyi tir da irin wannan kamakaryar da akeyi ma demokaradiyya, su kuma samar da wani horo me tsanani ga duk kasa da tayi irin wannan kashin mumuke ga demokaradiyya.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:01 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

XS
SM
MD
LG