Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Zargin Buhari Da Siyasa A Yaki Da Cin Hanci


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a Lokacin Da Ya Kama Hanyar Tafiya Afrika ta Kudu
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a Lokacin Da Ya Kama Hanyar Tafiya Afrika ta Kudu

Dokar da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya fitar na haramatawa wasu yan kasar su 50 fita zuwa kasashen wajen na cigaba da jawo cece-kuce a kasar.

Su dai wadannan mutane ana tuhumar su da yin ruf da ciki da kwanciyar magirbi da dukiyar kasa, abinda yasa aka umarci jami’an tsaro da su sa ido akansu don kada su samu damar sulalewa zuwa kasar waje.

Tun fako, wadansu jaridun kasar har sun buga sunayen wasu mutum 50 da dokar zata shafa, ciki har da matattu, to amma kuma sai daga baya fadar shugaban kasar ta musanta batun cewa an zayyano sunayen wadanda lamarin ya shafa.

Tuni ‘yan adawa suka bayyana daukar wannan matakin a matsayin siyasa, suka kuma bayyana daukar matakin a matsayin wani salon yakin neman zabe.

To sai dai kuma ,yayin da wasu ke zargin gwamnatin APC da bita da kulli da kuma wata manufa a yaki da cin hancin da rashawan, su kuwa kusoshin jam’iyar ta APC, na ganin ba haka lamarin yake ba.

Saurari cikakken rahoton Ibrahim Abdul’aziz

Martani Kan Hana Wadansu fita Daga Najeriya-3:25"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:25 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG