Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Aung San Suu Kyi Ta Ce Kasarta Ba Ta Da Laifi


Suu Kyi Yyain Da Take Jawabi
Suu Kyi Yyain Da Take Jawabi

Shugabar Myanmar Aung San Suu Kyi ta kare kasarta kan sukar da ta biyo bayan zartas da hukuncin da kotun kasar ta yi ma wasu 'yan jarida biyu masu aiki ma kafar labaran Reuters makon jiya, wadanda aka tuhume su da laifin saba ma dokar kiyaye sirrin gwamnati, dokar da aka kafa tun a zamanin mulkin mallaka.

An kama Wa Lone da Kyaw Soe Oo tun a watan Disamban bara bayan ganawarsu da wasu jami'an 'yan sanda biyu a wani wurin cin abinci a Yangon inda aka ba su wasu kundin bayanai. Su na binciken kashe wasu Musulmin 'yan kabilar Rohingya su 10 da 'yan sanda da soja su ka yi a kauyen Inn Din bara. An yanke ma 'yan jaridan biyu hukuncin daurin shekaru 7.

Da ta ke magana a babban taron kasa da kasa kan tattalin arziki wanda ake yi a Hanoi, babban birnin kasar Vietnam, Aung San Suu Kyi ta yi kira ga duk wanda ya soki lamirin hukuncin tare da kiran a saki 'yan jaridar, ciki har da Mataimakin Shugaban Amurka Mike Pence, da ya fito fili a bayyana inda aka yi rashin adalci a shari'ar.


Kungiyar kare hakkin Bil'Adama ta kasa da kasa Amnesty International, ta soki Aung San Suu Kyi saboda kare gwamnati kan hukuncin da aka yankewa 'yan Jaridar.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG