Mai magana da yawun kungiyar Houthi, Mohammed Abdelsalam ya ce, “Idan an samu cibaga a tattaunawar da za mu yi, wato cigaba wajen samun yarda da juna cikin aminci, da kuma tsarin da za a bi, za mu iya cigaba da wasu zagaye na tattaunawar" cikin watanni masu zuwa.
Wasu abubuwan da aka tabo a tattaunawar da Majalisar Dinkin Duniya ke daukar nauyin shiryawa, su ne musayar fursunoni da sake bude filin jirgin sama na Sanaa.
Wasu rahotanni sun ce bangarorin biyu sun amince da musanyar fursunoni kafin tattaunawar da za’a yi a Stolkham, amma, ba a sami wani cigaban kwarai ba akan wasu batutuwan.
Kamar batun bude filin jirgin saman Sanaa, da iko akan tashar jirgin ruwa na Hodeidah wanda shi ne mafi girma a kasar Yemen.
Za ku iya son wannan ma
-
Janairu 25, 2023
Mawakiya Yar Najeriya Ta Yi Tarihi A Bikin Bada Lambar Yabo Na Oscar
-
Janairu 13, 2023
Lisa Marie Presley, Diyar Mawaki Elvis Ta Rasu
-
Janairu 11, 2023
Ana Tsaftace Yankunan Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Ratsa A California
Facebook Forum