Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Babu Wanda Ya Illata Jikin Hanifa-Abdulmalik


Babu Wanda Ya Illata Jikin Hanifa-Abdulmalik
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:54 0:00

Babu Wanda Ya Illata Jikin Hanifa-Abdulmalik.

Shugaban Makarantar Noble Kids dake unguwar yan Kaba kwanar Dakata, a birnin Kano, Abdulmalik Mohammed Tanko, ya shaidawa Muryar Amurka cewa, ba gaskiya ba ne rahotannin da ake yayatawa cewa, sun yi gunduwa-gunduwa da jikin Hanifa Abdullahi bayan ta mutu kafin suka binne ta.

Abdulmalik wanda ake zargi da garkuwa da kuma kashe Hanifa, ya bayyana cewa, an sa Hanifa a cikin buhu ne wanda ba shi da girma sosai da ya zama dole kafarta ta tankware. Ya ce da yake ita karamar yarinya ce kuma buhun yana da fadi sai aka dan tankwara kafarta yadda dukan jikinta zai shiga buhun amma babu wanda ya dauki wuka ya illata jikinta.

Bisa ga cewarshi, tankware kafafunta kafin sa ta buhun da aka binne ta a ciki, ya sa lokacin da aka tono ta, aka ga kamar an karya gababuwanta, amma a Zahiri ba wanda ya daddatsa ta ko wani abu makamancin haka.

Gawar Hanifa da aka tono
Gawar Hanifa da aka tono

Ya kuma bayyana cewa, an cire rigar sanyi da baje, da kuma hijabin Hanifa ne daga jikinta bayan ta mutu, aka rika aikawa iyayenta a matsayin shaida domin neman kudin fansa. Dangane da lokacin, da kuma wurin da Hanifa ta rasu, Abdulmalik ya ce, ta kwana biyar a gidanshi tare da iyalinshi kafin ya fitar da ita zuwa wani wuri inda ta kwana daya, kafin ta cika ranar goma ga watan Disamba, watau kwana shida bayan yin garkuwa da ita.

A wata hira da aka yi da shi a baya, Abdulmalik ya bayyana cewa, babu wata alaka da ayyukan asiri a garkuwa da kuma kashe Hanifa. Bisa ga cewarshi, ya samu kanshi a cikin mawuyacin halin rayuwa ne, inda ake bin shi bashi da ya hada da kudin hayar ginin makarantar da kuma albashin ma’aikata, ya kuma rasa mafita, dalili ke nan da ya yanke shawarar yin garkuwa da Hanifa da tunanin samun kudin da zai fita daga matsalolin kudin da ya ke ciki.

Ya kuma bayyana cewa, ya yi amfani da Naira dubu saba’in da ‘yan kai daga cikin dubu dari da iyayen Hanifa suka fara bashi a matsayin kudin fansa kafin kama shi, wajen biyan kudin albashin ma’aikatan makarantar shi. Sai dai bai bayyana abinda ya yi da sauran canjin ba.

Wadanda aka tuhuma da kashe Hanifa Abdullahi a Kano
Wadanda aka tuhuma da kashe Hanifa Abdullahi a Kano

Shi dai abokin shi, wanda a da, yake aikin gadi a makarantar, Hashimu Ishiyaku, ya bayyana cewa, Abdulmalik ya biya shi Naira dubu daya domin haka rami da kuma binne Hanifa da ya yi.

Da aka tambaye shi yadda ya ke ji da aka kai shi kotu, Abdulmalik ya bayyana cewa, tun kafin kawo shi kotu ya shiga halin kakanikayi. Yace ya shiga hali na tashin hankali, domin duk wanda ya san shi a baya, ya san shi ba mutum ne mai son tashin hankali ba. Abdulmalik ya bayyana cewa, lamarin ba abu ne na jin dadi ba. Ya kuma tabbata su ma (iyayen), ba zasu ji dadi ba.

Mahaifiyar Hanifa da mahaifiyarta. (VOA/Instagram)
Mahaifiyar Hanifa da mahaifiyarta. (VOA/Instagram)

Dangane da kama shi da kai shi kotu, Abdulmalik ya ce, “tun ma kafin a kawo ni kotu, na riga na yanke shawarar cewa, zan fito bisa radin kaina in fada. Kuma tunda na fito na yi haka abinda na ke jira in gani shine kawai kotu ta tabbatar da adalci irin na ta.”

Abdulmalik Mohammed Tanko, ya yi garkuwa da Hanifa Abubakar ‘yar shekar biyar ne ranar 4 ga watan Disamba ta wajen daukar ta a keke Napep, tana kan hanyar komawa gida bayan tashi.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG