Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Bangaren Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Na Zargin PDP Da Shishshigi


Shugaban Nijeriya Goodluck Jonathan
Shugaban Nijeriya Goodluck Jonathan

Mataimakin Shugaban bangaren Kungiyar Gwamnonin Nijeriya na zargin jam'iyyar PDP mai mulkin Nijeriya da yin katsalandan a zaben kungiyar na kwanan nan

Bangaren kungiyar Gwamnonin Nijeriya na zargin jam'iyyar PDP mai mulkin Nijeriya da shishshigi a zaben kungiyar na kwanan nan.

A hirarsu da wakilinmu na shiyyar Sakkwato, Murtala Faruk Sanyinna, Mataimakin Shugaban bangaren kungiyar Gwamna Abdul'aziz Yari Abubakar na jihar Zamfara ya ce dukkannin gwamnonin 35 sun kada kuri'unsu kuma gwamna Rotimi Amaechi na jihar Rivers mai samun goyon bayan mafiya yawan gwamnonin ya ci da kuri'u 19, yayin da shi kuma Gwamna Jonah Janga na jihar Filato mai samun goyon bayan jam'iyyar PDP ya sha kasa da kuri'u 16.

Gwamna Abubakar ya ce bangaren su gwamna Jang ba su ma da Sakatariya, kuma ba da dadewa ba gwamnonin za su hada kawunansu saboda kungiyar na da muhimmanci ga kowannensu.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:18 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG