Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Bikin Kaddamar Da Cibiyar Kasuwancin Albasa a Nijar


Albasa
Albasa

A Jamhuriyar Nijer an bude bikin kaddamar da wata cibiyar kasuwancin albasa a birnin Yamai da nufin karfafa hanyoyin baiwa manoman albasa da masu kasuwancinta damar cin moriyar wannan sana’a.

Wannan sana'a ta sa Nijir din ta yi fice a kasashen waje saboda ingancin albasar da ake nomawa a karkarar Galmi dake jihar Tahoua.

Noman albasa na kan gaba a sahun ayyuka da sana’oin da suka fi samar da kudaden shiga a kasar Nijar amma lura da yadda abubuwan ke gudana cikin wani yanayi irin na karazube ya sa shugabannin manoma da masu kasuwancin albasa kafa cibiyoyin kasuwancin albasa a wasu mahimman wurare cikinsu har da birnin Yamai.

Wannan na matsayin wani matakin share fage a yunkurin soma sarrafa albasa zuwa wasu nau’o’in cimaka na daban.

Ta wani bangaren cibiyoyin kasuwancin albasa wani tsari ne da ke hangen takaita ko kuma kawo karshen asarar da manoman albasa da masu kasuwancinta ke tafkawa saboda yadda a can baya harakokin ke gudana a gargajiyance inji Alhaji Abdulkader Issaka shugaban cibiyar kasuwancin albasa ta birnin yamai.

Shugaban kungiyar manoman albasa daga tarayyar Najeriya da ya jagoranci wata tawagar manoman albasa a taron kaddamar da wannan cibiya yace sun zo da wasu mahimman shawarwari.

Ga Souley Moumouni Barma da karin bayani:

Bikin Kaddamar Da Cibiyar Kasuwancin Albasa a Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:04 0:00


Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG