A yau Laraba Wakilan tattaunawa na Birtaniya da Kungiyar Tarayyar Turai suka bayyana ra’ayoyi da suka ci karo da juna akan ficcewar Birtaniya daga Kungiyar Tarayyar Turai, bayan da majalisar dokokin Birtaniya ta ba Fira minista Theresa May umarnin sauye yarjejeniyar ficcewar.
Wasu jerin kuri’un da aka kada a zauren Majalisar Birtaniya a jiya Talata sun amince da shirin jam’iyar May na neman wata yarjejeniyar.
A cikin wata hira a yau Laraba, Ministan Birtiniya mai kula da harkokin ficcewar Birtaniya daga Kungiyar Tarayyar Turai, Stephen Barclay ya fada wa kafar yada labarai ta BBC cewa sauye-sauye ne zai zama maudu’in tattaunawar da za a fara a ‘yan kwanaki masu zuwa.
Amma daga bangaren Kungiyar Tarayyar Turai, wakilin tattaunawar su Michel Barnier ya ce sun riga sun bayyana nasu ra’ayin
Za ku iya son wannan ma
-
Maris 21, 2023
Saudiyya Ta Ce Ranar Alhamis Watan Azumi Zai Kama
-
Maris 17, 2023
Kotun ICC Ta Ba Da Izinin Kama Putin
-
Maris 13, 2023
Shugaba Buhari Ya Taya Xi Jinping Murnar Sake Lashe Zabe
-
Maris 08, 2023
Ana Bikin Ranar Mata A Duniya
Facebook Forum