Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Bom ya Fashe A Jos


Jos Blast, Najeriya ( File Photo)
Jos Blast, Najeriya ( File Photo)

Misalin karfe shida da rabi ne agogon Najeriya, boma-boman suka fashe a babbar kasuwar birnin Jos dake arewacin Najeriya.

Wakiliyar Dandali Zainab Babaji ta samu bayanai dake cewa a kalla mutane 7 ne suka rasa rayukansu, wasu kuma suka jikkata.

Ya zuwa yanzu, babu wanda ya dauki alhakin harin, amma a baya-bayannan an zargi kungiyar tayar da kayar baya, Boko Haram da kai hare-hare a duk fadin arewacin Najeriya.

XS
SM
MD
LG