Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Cikin Watanni 18 Mutane Dubu Goma Suka Mutu A Yakin Yemen - MDD


Sarki Salman na Saudiya da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Sarki Salman na Saudiya da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

A yau Talata ne Majalisar Dinkin Duniya ko MDD ta bada adadin mutanen da aka kashe a Yemen cikin watanni 18 zuwa dubu goma, a yayind da fadar ke ci gaba da jefa miliyoyin yan Yemen cikin tsananin bukatar taimakon agajin gaggawa

Shugabar sashin bada agaji na MDD Jamie McGoldrick tace tana yiwuwa wa’yannan akaluman su fi abin da aka bayyanar.

Kafin yau Talata, jami’an MDD suna fadin akalla mutane dubu shida ne suka mutu a wannan yakin kungiyar ‘yan tawayen Houthi dake samun goyon bayan Iran. ‘Yan tawayen suna adawa ne da gwamnatin shugaba Abdu Rabu Mansour Hadi ne.

Bugu da kari akan wannan yakin basasa da ake kai hare-haren sama karkashin jagorancin Saudiya bai taimakawa gwamnati ba, saboda Yemen tana fama da hare-haren yan bindiga ciki har da wanda ya faru a ranar Litinin a Birnin, a tashar jirgin ruwa ta Aden dake kudancin kasar.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG