Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Clinton Ta Ce Mutuwar Maharin Ofishin Jakadanci Babban Cikas Ne Ga Al-Ka'ida


U.S. Secretary of State Hillary Clinton waves on arrival at Julius Nyerere International Airport in Dar es Salaam, Tanzania, June 11, 2011.
U.S. Secretary of State Hillary Clinton waves on arrival at Julius Nyerere International Airport in Dar es Salaam, Tanzania, June 11, 2011.

Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka Hillary Clinton ta ce mutuwar Fazul Abdullah Mohammed, wanda ake zargi da jagorantar harin da aka kai a Ofishin Jakadancin Amurka a gabashin Afirka a 1998, ta sa al-Ka’ida sake samin cikas.

Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka Hillary Clinton ta ce mutuwar Fazul Abdullah Mohammed, wanda ake zargi da jagorantar harin da aka kai a Ofishin Jakadancin Amurka a gabashin Afirka a 1998, ta sa al-Ka’ida sake samin cikas.

Hukumomi a Somaliya sun fadi ran Asabar cewa an kashe jigon na al-Ka’ida kwanaki biyar da su ka gabata a wani wurin duba ababen hawa da ke cikin birnin Mogadishu.

Misis Clinton, wadda ke ziyarar aiki a Tanzania, t ace mutuwar Fazul itace babbar asara ta biyu da al-Ka’ida ta yi tun bayan da dakarun Amurka na musamman suka kashe Osama bin Laden a watan jiya.

Kungiyar ta al-Ka’ida ta kai hari kan Ofisoshin jakadancin Amurka a Nairobin Kenya da Dar es Salam din Tanzania ran 7 ga watan Agustan 1998, suka hallaka mutane 224.

Ran Lahadi, Sakatariya Clinton ta age fulawa a wurin tuna ‘yan Tanzaniya 12 din da aka kashe a harin bom din Dar es Salam.

XS
SM
MD
LG