Ma’aikatar lafiya a Sudan, ta ba da rahoton samun mutum na farko da ya mutu sanadiyyar cutar ta coronavirus.
Ma’aikatar ta ce wani mutum mai shekara 52 ne ya gamu da ajalinsa bayan da ya dawo daga wata ziyara da ya kai Hadaddiyar Daular Larabawa a ranar Alhamis.
Tuni dai hukumomi a Sudan din suka nemi jama’ar kasar da su fara daukan matakan kariya domin dakile yaduwar cutar, ta hanyar wanke hannayensu akai-akai da sabulu,.
Sannan an umurce su da su sanar da hukumomi da zaran sun ga wani da ake fargabar ya kamu da ita.
A halin da ake ciki, hukumomi a kasar ta Sudan, sun haramta zirga-zirgar motocin sufuri na bas-bas da ke kai wa da komowa tsakanin Sudan da Masar, sannan sun haramta saukar jiragen da suka fito daga kasashen da aka samu bullar cutar.