Hukumomi a kasar Botswana sun ce baki dayan ‘yan majalisun kasar da suka hada har da shugaban majalisar dattawa da ta wakilai suna a cikin zaman kulle na tsawon kwanaki 14 daga yau Juma’a, kwana daya bayan wani gwaji da aka sami wani jami’in kiwon lafiya na majalisar ya kamu da cutar Coronavirus.
Wata sanarwar gwanatin ta ce jami’in na cikin mutane na 7 sababbin kamuwa da cutar a kasar da ke yankin kudancin Afrika, wanda ya kara adadin masu cutar a kasar zuwa 13.
Shugaban kasar Eric Masisi, ya koma bakin aikin tun a farkon watan nan na Afrilu, bayan killace kansa da yayi, sakamakon wani balaguro da yayi a makwabciyar kasar Namibiya a watan da ya gabata. To sai dai an gwada shi ba ya dauke da cutar ta COVID-19 a ran daya ga watan Afrilu.
Tuni da Masisi ya kafa dokar gaggawa tare da dukar matakan hana yaduwar cutar, wadda ta yi sanadiyyar mutuwar mutum daya.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 26, 2021
Gwamnatin Nijar Ta Mayar Da Martani Game Da Tarzomar Zabe
-
Fabrairu 25, 2021
An Kama Masu Zanga Zanga Sama Da 200 a Nijar
-
Fabrairu 25, 2021
Ghana Ta Sami Kason Farko Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 23, 2021
NIJAR: Bazoum Mohamed Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa
-
Fabrairu 23, 2021
Wai Ko Wa Ake Ganin Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa A Nijar?
-
Fabrairu 22, 2021
Ana Jimamin Mutuwar Jami'an Zabe Bakwai Da Suka Rasu a Nijar
Facebook Forum