Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

COVID-19: 'Yan Ci Rani Na Fuskantar Rashin Tabbas A Thailand


Wasu 'yan ci rani a kasar Thailand
Wasu 'yan ci rani a kasar Thailand

Ma’aikata ‘yan cirani da su ka makale a Thailand tun bayan kafa dokar takaita zirga-zirga a watan Maris, na fuskanta makoma marar tabbas da kuma tsadar rayuwa, duk kuwa da tallafin da gwamnatin kasar ke bai wa leburori marasa ayyukan yi a kasar.

‘Yan kwanaki kawai bayan kafa dokar bayar da tallafin gaggawa ranar 23 ga watan Maris, kasar Thailand ta yi shelar rufe dukkan iyakokinta, ta kuma yi shelar shirin bayar da tallafi ga ma’aikatan da dokar takaita zirga-zirgar ta shafa – walau ‘yan asalin Thailand din ko baki.

To amma sharuddan samun tallafin sun hada da mallakar asusun banki, da kuma shaidar an bayar da gudunmowa ga gidauniyar gwamnati na tsawon akalla wata shida, wanda hakan ya kai ga ware mafiya talauci, ciki har da miliyoyin ‘yan cirani da su ka zo daga kasashe makwabta.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG