Firai Ministan kasar China, Li Leqiang ya kai ziyara birinin Wuhan a yau Litinin, domin haduwa da jami’an lafiya da kuma duba matakan da aka dauka game da barkewar cutar ta Corona virus da ta kashe mutune 81.
Wuhan, shi ne birnin da cutar ta barke, kuma an gindayawa mutanen birnin da wasu sauran garuruwa tsauraran matakan zirga zirga yayin da gwamnati ke kokarin dakile yaduwar cutar.
Jami’ai sun dauki karin wasu matakai a jiya Lahadi, da suka hada da kara hutun sabuwar shekara da kwanaki 3 don su rage cudanyar mutane da yawa.
Li Bin, wanda shi ne kwamishinan lafiya a China, ya ce, "Wannan cuta sabuwa ce a gare mu, ba mu da cikakken bayani game da ita kuma har yanzu ba mu samu kwararan bayanai game da ita ba."
Sabbin alkaluman da jami’an hukumomin kiwon lafiya na China suka tattara sun hada har da sama da mutune 2,700 da suka kamu da cutar.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum