Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Cutar Korona: Jami’an Tsaro Sun Killace Fadar Mai Martaba Sarkin Daura


 Sarkin Daura Mai Martaba Dr. Umar Faruk a fadarsa
Sarkin Daura Mai Martaba Dr. Umar Faruk a fadarsa

A wani al'amari mai karkada hanji game da wannan mugunyar cutar nan ta korona, wata gamayyar jami’an tsaron Najeriya ta killace Fadar Mai Martaba Sarkin Daura da daren jiya Asabar saboda rade-radin shigar cutar fadar.

Bayan da labarin killace fadar ya fara bazuwa, wakilin Sashen Hausa a yankin, Sani Malumfashi ya tuntubi wasu majiyoyi masu tushe, wadanda su ka tabbatar masa cewa lallai su ganau ne game da killace fadar Mai Martaba Sarkin Daura da aka yi saboda fargabar cewar cutar korona ta kutsa cikin fadar kamar yadda aka ce ta shiga wasu gidaje a garin Daura.

Ga wakilin Sashen Hausa na Muryar Amurka a shiyyar, Sani Shu'aibu Malumfashi da abin da ya kalata:

please wait

No media source currently available

0:00 0:00:56 0:00


Facebook Forum

XS
SM
MD
LG