Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dakarun Najeriya Sun Dakile Harin Boko Haram a Bama


Wani wuri da mayakan Boko Haram suka kai hari a arewa maso gabashin Najeriya
Wani wuri da mayakan Boko Haram suka kai hari a arewa maso gabashin Najeriya

Rahotanni sun ce harin ya kai ga musayar wuta tsakanin dakarun Najeriya, lamarin da ya sa aka samu mace-mace a bangarorin biyu.

Mayakan Boko Haram sun kai wani hari akan dakarun Najeriya a Rann da ke karamar hukumar Kala-Balge a jihar Bornon kasar.

Rahotanni sun ce harin ya kai ga musayar wuta tsakanin dakarun Najeriya da maharan, lamarin da ya sa aka samu mace-mace a bangarorin biyu.

Harin ya faru ne a ranar Alhamis, amma hukumomin tsari ba su ce komai dangane da harin ba.

A daya bangaren kuma, dakarun kasar ta Najeriya, sun dakile wani hari na daban da ‘yan kungiyar ta Boko Haram suka kai a garin Bama.

Bama shi ne garin da kungiyar ta taba ayyanawa a matsayin hedkwatarta, ta kuma taba karbe ikonsa daga dakarun Najeriya.

Amma an kwato garin a watan Maris din 2015.

Jaridun Najeriya da dama da suka ruwaito labarin sun ce jama’ar garin na Bama sun yi ta murna bayan da aka fatattaki mayakan na Boko Haram.

Facebook Forum

Wata manhaja mai saukaka wahalar samun gidan abinci na halal ga Musulman dake zaune a kasashen Turai
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:21 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG