Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

ETHIOPIA: An Cafke Mutane 30 Akan Bam da Ya Tashi a Wurin Gangamin Siyasa a Addis Ababa


Gangamin goyon bayan Firai Ministan Habaha Abiy Ahmed,
Gangamin goyon bayan Firai Ministan Habaha Abiy Ahmed,

Shugaban 'Yan sandan kasar Habasha ko Ethiopia, Zeinu Jemal ya sanar da cafke mutane 30 dangane da tashin bam a wani gangamin siyasa da ya yi sanadin mutuwar mutane biyu

An cafke mutum 30 da ake zargi na da hannu a wata fashewa da ta auku a wani gangamin siyasa a Addis Ababa, wacce ta yi sanadin mutuwar mutum biyu a cewar kafar yada labarai mallakar gwamnatin Habasha, wacce ta ruwaito labarin daga wasu majiyoyin ‘yan sanda.

Adadin wadanda ake zargi da hannu a wannan hari da aka kai da gurneti, ya haura mutum shida da aka kama a baya.

Yayin wata hira da ya yi da kafar yada labarai ta gwamnatin Habasha, shugaban ma’aikatar ‘yan sandan tarayya, Zeinu Jemal, ya ce “adadin wadanda ake zargi a harin wanda aka kai a wani wuri da ake kira Meskel Square ya kai 30, amma ba tare da ya yi cikakken bayani.

Jami’ai sun ce mutum 150 suka jikkata a fashewar, yayin da ma’aikatar lafiya ta ba da tabbacin karin mutuwar mutum na biyu a jiya Lahadi.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG