Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gasar AFCON: Najeriya Ta Doke Kamaru, Za Ta Kara Da Angola A Kwata Fainal


Ivory Coast AFCON Soccer
Ivory Coast AFCON Soccer

Tawagar Super Eagles ta Najeriya ta doke Kamaru da ci biyu da nema a wasan zagaye na biyu na gasar cin kofin nahiyar Afirka ga suka buga a ranar Asabar.

Ademola Lookman mai buga wa kungiyar kwallon kafa ta Atalanta a kasar Italiya ne ya zura wa Najeriya kwallaye biyu. Daya kafin a tafi hutun rabin lokaci na biyu bayan an dawo hutu a misali minti 90 na wasan da ake bugawa a kasar Kwaddebuwa.

Hakan na nufin Kamaru ta fita da gasar kuma Najeriya za ta fafata da Angola, wadda ta fitar da Namibiya, a dayan wasan da aka buga a ranar Asabar.

A dayan wasan kuma, dan wasan Angola, Gelson Dala ne ya zura kwallaye - biyu kafin a tafi hutun rabin lokaci.

Da aka dawo kuma Agostinho Mabululu ya zura kwallo ta uku.

Wasan ya yi zafin da sai da alkalin wasa ya ba kowane bangaren jan kati - abin da ya sa dukkan su suka buga wasan da 'yan kwallo goma-goma.

Mabululu ya kafa tarihi a Angola na zama dan wasan kasar na farko da ya taba cin kwallaye uku a gasar kofin nahiyar Afirka.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG