Gobarar dajin dake ake fama da ita a Arewacin jihar California ta Amurka, ta ci gaba da fadada a jiya Laraba, lokacin da iska ke kara rura wutar, abinda ya tilastawa jami’ai kwashe mutanen dake yankin wutar.
Masu hasashen yanayi sunce a yau Alhamis za a samu karin iska mai karfi yankin Arewacin California, wanda zai sa duk wani kokarin shawo kan wutatai har guda 22 dake ci a Arewacin birnin San Francisco, ya fuskanci wahalar samun nasara.
Jami’ai sunce izuwa yanzu mutane 21 ne suka mutu wasu kuma sama da 300 an neme su an rasa duk a dalilin gobarar. Layikan wutar lantarki da suka fado na ci gaba da kasancewa akan titunuan unguwannin da wutar ta lakume, yayin da ‘yan kwana-kwana ke kokarin kashe gobarar.
‘Yan Sanda sun rufe hanyoyi masu yawa domin hana mutane shiga yankunan da gobarar ta lalata, wadanda suka hada da hekta dubu 69 a cikin yankunanb kananan hukumomi da daman a jihar
Facebook Forum