Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

GRACE ALHERI ABDU: Me Ya Kai Sanata Da Marin Mata? Kashi Na Daya-Yuli,11, 2019


Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu

A karshen makon da ya gabata aka yi ta yayata faifan bidiyon da aka nada inda aka ga dan majalisar dattijai mai wakiltar Adamawa ta arewa a majalisar dattijan Najeriya Elisha Abbo ya rika kakkale wata mace da ke aiki a shagon da mari ya kuma umarci dogarinsa dan sanda ya kama ta. Sai dai ganin yadda aka yi ta zanga zanga da tofin Allah tsine kan batun, dan majalisan ya fito ya bada hakuri yana kuka yana neman gafara.

Shirin Domin Iyali ya tattauna da wadansu mata 'yan gwaggwarmaya dake zaune a nan Amurka Helen Bako dake jihar California da kuma Khuraira Musa wadda ke zaune a birnin NY domin jin matakan da za a iya dauka na ganin haka bata sake faruwa ba.

Saurari bayanan nasu

Sanata da cin zarafin mata-10:00" Pt1
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:32 0:00

.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG