Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, ya yaba da ci gaban da ake samu a fagen siyasar Sudan, yayin da gwamnatin wucin gadin da aka kafa take kafa turakun dimokradiyya.
A jiya Juma’a Guterres ya nuna matukar farin cikinsa, yana mai cewa “ranar Juma’a rana ce ta musamman a gare shi, domin ba kasafai ake samun labari mai dadi a taron Majalisar Dikin Duniya ba.”
“Wannan lokacin ne da na fi farin ciki a wannan taron cikin wannan mako. Idan da za a ce shekara daya da ta wuce akwai yiwuwar wannan zama, ban yi tsammanin akwai wanda zai yarda ba. Amma abin farin ciki shi ne ga shi muna bikin kafa sabuwar Sudan.” Inji Guterres.
Sai dai ya ce kafa gwamnatin wucin gadin, mafarin tafiyar ce, ba karshenta ba.
Guterres da kungiyar Tarayyar Afirka, sun yi kira da a dage takunkuman da aka sakawa kasar sannan Amurka ta cire ta daga jerin kasashen da ke marawa ayyukan ta’addanci baya.
Za ku iya son wannan ma
-
Janairu 26, 2021
An Kama Makamai a Jihar Tahoua a Nijar
-
Janairu 25, 2021
'Yan Ta'adda Sun Kashe Sojoji A Kasar Mali Tare Da Jikata Wasu
-
Janairu 24, 2021
An Kashe Mayakn Al-Shabab 189 A Wani Samame Da Aka Kai A Mabuyar Su
-
Janairu 23, 2021
An Kama Wani Direban Motar Asibiti Dauke Da Lodin Tabar Wiwi a Nijer
-
Janairu 18, 2021
'Yan Adawa A Uganda Sun Ki Yarda Da Sakamakon Zaben Ranar Lahadi