Gwamnan jihar Neja, Alhaji Abubakar Sani Bello ya bayyana takaicin hukuncin da aka yankewa wasu mazauna gidan yari da suka aikata kananan laifukka.
Gwamnan Abubakar Sani Bello ya bayyana takaicin ne sai’lin da ya kai ziyara a gidan yarin garin Kontagora dake cikin jihar ta Niger.
Gwamnan jihar ta Neja yace bai dace ana cusa mutane gidan yari na tsawon lokaci ba, ba tare da an yanke musu hukunci ba.
Yace yaga wadanda suka dauki shekara da shekaru gidan yarin ba tare da yanke musu hukuncin laifukkan da suka aikata ba.
Gwamnan yace wasu sun yi shekaru 4, wasu 2, wasu ko har shekaru 6 da sunan jiran hukunci, abinda yace wannan bai dace ba.
Da Wakilin Muryar Amurka Mustapha Nasiru Batsari ya tambaye shi ko akwai wadanda zasu ci gajiyar wannan ziyar tasa, sai Gwamnan yace, kwarai da da gaske kuwa.
Ga Mustapha Nasiru Batsari da karin bayani2'59
Facebook Forum