Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Ukraine Zata Murkushe Borin 'Yan Tawaye


'Yan tawaye dake goyon bayan yankinsu ya hade da kasar Rasha
'Yan tawaye dake goyon bayan yankinsu ya hade da kasar Rasha
Gwamnatin kasar Ukraine ta ce Jumma'annan zata kawo karshen mamaye gine-ginen gwamnatin da 'yan aware masu goyon bayan Rasha suka yi a kusa da kan iyakar Rasha, ko ta hanyar tattaunawa ko ta hanyar yin amfani da karfi.

Da ya ke magana game da kiki-kakar da ake yi a biranen gabashin kasar na Luhansk da Donetsk, ministan harakokin cikin gidan kasar Ukraine, Arsen Avakov, ya fada a jiya Laraba cewa :" masu son a tattauna, mu na yi mu su tayin tattaunawa da kuma warwarewa ta hanyar siyasa, 'yan tsirarun da ke son fada kuma, za su samu amsa mai tsananin karfi."

A jiya Laraba gwamnatin kasar Ukraine ta yi wannan kashedi, a lokacin da jami'ar diflomasiyar Amurka, Victoria Nuland ta shaidawa wani kwamitin majalisar dokokin Amurka cewa a tsanaki aka shirya mamaye gine-ginen, cikin kyakkyawan tsari, da kuma sanin wuraren da ya kamata a zaba. Haka kuma ta ambaci kwakkwarar shaidar cewa da hannun Rasha a ciki, sannan ta yi gargadi game da abun da zai biyo baya idan aka bari aka yi rikicin ba a shawo kan sa ba.
XS
SM
MD
LG