Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Najeriya Ta Kulla Yarjejeniya Da Tsagerun Niger Delta


Wani Bututun Mai Da Aka Fasa
Wani Bututun Mai Da Aka Fasa

Gwamnatin Najeriya ta cimma shirin tsagaita wuta da tsagerun Niger Delta da ke kai hare-hare akan bututan man man kasar, a cewar wani babban jami’in kamfanin matatar man kasar a hirar da ya yi da Muryar Amurka a yau Talata.

Sai dai mayakan kungiyar Niger Delta Avengers ta musanta cimma wata matsaya da gwamnati, inda ta rubuta a shafinta na Twitter cewa, zancen ba shi da tushe ballantana makama.

Kungiyar dai ta sha daukan alhakin kai hare-hare akan bututan man kasar, lamarin da ya kassara yawan man da kasar ke fitarwa mai yawan ganga miliyan biyu a kowace rana.

Masana tattalin arziki sun alakanta matsalar tabarbarewar tattalin arzikin da Najeriyar ke fuskanta da aika-aikan da tsegerun na Niger Delta ke yi.

Najeriya ita ce kasar da ta fi kowace samar da man fetur a nahiyar Afrika.

Labarin cimma matsayar tsagaita wutar, ya samo asali ne tun bayan da ministan man fetur din kasar Ibe Kachikwu ya kai ziyara yankin na Niger Delta.

XS
SM
MD
LG