Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Tallafa Ma ‘Yan Gudun Hijirar Boko Haram


Wasu 'yan gudun hijirar Boko Haram
Wasu 'yan gudun hijirar Boko Haram

Gwamnatin Najeriya ta tashi haikan wajen karfafa gwiwar 'yan gudun hijirar Boko Haram da ke komawa gidajensu da su ka gudu su ka bari.

A yinkurinta na sake tsugunar da ‘yan gudun hijirar Boko Haram da ke dawowa garuruwansu, gwamnatin tarayyar Najeriya ta shiga samar masu da tallafi gadan-gadan a wuraren da su ke a fadin kasar.

Sakataren Gwamnatin Tarayyar Najeriya, wanda hadimin Shugaban kasa Ibrahim Baba Fatel ya jagorance ci ya ce abin da gwamnati ta sa gaba a yanzu shi ne sake tayar da komadar masu dawowar.

Wasu daga cikin ‘yan gudun hijirar da ke dawowar sun ce abubuwa sun fara kyautatuwa, to amma har yanzu sun a fama da karancin kayan bukata. Don haka sun yi kira ga gwamnatoci da sauran wadanda abin ya shafa da su tashi haikan wajen agaza masu.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:53 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG