Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatoci Na Cigaba Da Mayar Da Almajirai Jihohinsu Na Asali


Wasu almajirai
Wasu almajirai

A yayin da jihohi suka fara daukar matakan mayar da almajirai jihohinsu na asali, mazauna Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, Abuja sun fara nemar bayani a kan matakin da Minista Muhammad Bello zai dauka a kan almajirai da jihohi za su iya maida gida, Abuja.

Batun almajiranci, abu ne da ya jawo cece-kuce tsakanin al’umman jihohin arewa da dama, inda yawanci masana a fannin ilmin addinin islama ke yin tir da salon koyar da almajirai na zamanı da aka hada da barace-barace, sabanin yadda ya ke kafin lokacin mulkin mallaka.

A cikin tarihin arewacin Najeriya kafin lokacin mulkin mallaka, ba a san almajirai da yin barace-barace ba, lamarin da wasu daga cikin al’umman Najeriya ke dangantawa da rashin iya jagoranci, maida sarautar gargajiya karkashin ikon kananan hukukomi da dai sauransu.

Almajiri
Almajiri

A lokacin da cutar korona ke cigaba da yi wa jihohin Najeriya katutu, mazauna Birnin Tarayyar Najeriya, Abuja sun fara kokawa a kan yadda aka bar almajirai a baya wajen kulawa.

Cikin masu kokawar har da wani fitaccen marubuci a fannin addini, Ghazali Muhammad Mijinyawa, wanda ya bayyana cewa nauyin kula da almajirai ya dogara ne a kan iyaye, shugabanni da asuran masu ruwa da tsaki.

Haka kuma, wani malami a makarantar boko da arabiyya na An-noor, Muhammad Sagir Assalafi, ya danganta kai yara almajiranci da iyaye ke yi da talauci inda ya bukaci gwamnati ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na tallafa wa iyayen wadannan yara.

Shi ko wani almajiri dake karatun Arabiyya a yankin Mpape na Abuja mai suna Muhammad Muhammad ya ce bai san ko mene ne cutar covid-19 ba, kuma idan gwamnatin zata maida shi Kano wajen iyayensa, zai yi farin ciki matuka.

Duk kokarin ji ta bakin Ministan Birnin Tarayya, Abuja dai ya ci tura.

A cikin littattafan tarihi dai, Kalmar almajiri ya samo asali ne daga kalmar Larabci ta “Almuhajiru” dake nufin dan cirani mai neman ilmi, kuma daga masarautar Borno aka faro, inda a baya ba a bautar da yara almajirai.

A baya-bayan nan ne gwamnati ta mayar da almajirai sama da ashirin gida Kaduna inda akalla 21 suke dauke da kwayar cutar covid 19.

Ga Halima Abdulrauf da cikakken rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:01 0:00


Facebook Forum

XS
SM
MD
LG