Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Har Yanzu Da Sauran Rina A Kaba A Majalisa- Abu Ibrahim


Sanata Bukola Saraki, sabon shugaban Majalisar Dattijai, Yuni 9, 2015.
Sanata Bukola Saraki, sabon shugaban Majalisar Dattijai, Yuni 9, 2015.

Bayan fiye da watanni biyu da kaddamar da majalisun tarayyar Najeriya, majalisun basu yi zaman da ya kai na makonni uku ba biyo bayan rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyar APC mai mulki.

Bayan dinke wannan Baraka ne majalisun suka sake lale wajen maida hankali kan abinda suka ce yana ciwa talakawa tuwo a kwarya. Tare da cin alwashin marawa shugaba Muhammadu Buhari baya a yunkurinshi na ganin ya cimma burinsa na yaki da cin hanci da rashawa da bunkasa kasa.

Ko da yake ana ganin an sami masalaha a majalisar ganin yadda aka rika tada jijiyar wuya da kuma ba hammata iska a farkon tafiyar majalisar, wadansu ‘yan majalisar sunce har yanzu tana kasa tana dabo sai dai kasancewarsu dattawa, zasu ci gaba da kokarin ganin an gyara.

A cikin hira da Muryar Amurka ‘yan majalisa da dama sun bayyana kudurin majalisar na tunkarar matsalolin da suka addabi talakawan kasar, musamman matsalar tsaro da ake fama da ita a arewacin Najeriya inda kungiyar Boko Haram ke ci gaba da tada kayar baya.

Wakiliyarmu Madina Dauda na dauke da ci gaban rahoton.

Rahoton Madina Dauda-2:53"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:53 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG