Hukumomi a birnin tarayya na nuna damuwa dangane da yadda mutane ke tayin tururuwa suna shiga birnin tarayya domin neman mafaka. Mun samu zantawa da Alh. Abbas Idris, shugaban hukumar taimakon gaggawa FEMA ta birnin tarayyar Abuja, a wata ziyara da yakawo ma sashen Hausa a nan birnin washintan.
Yayi muna Karin haske dangane da kokarin hukumar su tare da hadin gwiwa da wasu hukumomin, ta yadda suke taimakama mutane da suke a birnin tarayya, don gudun hijira.
Yace hukumar suna ziyartar mutanen da ke gudun hijira a birnin tarayya da suka kai wajaje 4 wanda kuma suna basu abinci da magunguna, har ma da ilmantar da ‘yayan masu gudun hijira. Kuma dangane da har kar tsaro suna kokarin tantance wadanda suke da bukata na gurin zama, don kada su hade da mugayen mutane. Ya kara da cewar Ministan birnin tarayya ya bada wuri da za’a gina ma mutanennan wurin zama na kankanin lokaci, wanda yanzu haka an fara aikin. Ya kuma yi kira da babbar murya da cewar duk ilahirin mutane su manta da banbancin addini ko kabilanci don neman zaman lafiya da cigaban kasar baki daya.