Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar habaka Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka, ECOWAS, Ta Kuduri Aniyar Hana Barace-Barace a Yankin


Shugabannin ECOWAS
Shugabannin ECOWAS

[Hukumar habaka Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka na ganin lokaci ya yi da za’a haramta yin barace-barace a cikin kasashen tare da karkata akalar masu baran kan hanyoyin dogaro ga kai

Duk da cewa babu wasu alkalumman dake fayce adadin mabarata a kasashen yammacin Afirka, Hukumar ta ECOWAS tana ganin lokaci ya yi da za’a haramta barace barace domin a dora almajirran akan hanyar neman na kai ta hanyar sana’a.

‘Yar Majalisar Dokoki, Halima Mamman mai wakiltar Jumhuriyar Nijar, ta ce idan aka duba kasashen Inyamurai ko Benin babu mai bara sai dai a same su a cikin ‘yan arewacin Najeriya da kasar Nijar. Tace ko addini da yace a yi bara, ya jadadda a yi ne daidai abin da mutum zai ci. kuma da zara ya samu kamata ya yi ya koma gida. Amma yanzu wasu sun maida ita sana’ar tara dukiya.

Ga rahoton Souley Barma da karin bayani

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:17 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG