Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar Kididdiga Ta Ce An Rage Haihuwa A Nijar


Taron Fadakar Da Mata Tasirin Tsarin Iyali A Ranar Mata Ta Duniya.
Taron Fadakar Da Mata Tasirin Tsarin Iyali A Ranar Mata Ta Duniya.

Hukumar kididdigar jamhuriyar Nijer ta bayyana gano raguwar haifuwa a kasar sakamakon yadda jama’a su ka fara amincewa da matakan tsarin iyali.

Sai dai a daya bangare mutuwar yara ‘yan kasa da shekara daya da haifuwa ta karu saboda haka hukumar ta shawarci mahukunta akan bukatar gudanar da bincike domin gano zahirin dalilan da ke haddasa wannan matsala.

A binciken da tace ta gudanar daga shekarar 2019 zuwa 2021 hukumar kididdiga ta kasa wato INS a rahoton da ta gabatar a yayin wani bukin musamman tace an samu ci gaba sosai a yunkurin ganar da jama’a mahimmancin shimfida tsarin iyali a Nijer idan aka kwatanta da yanayin da ake ciki a shekarar 2012.

Hukumar ta INS na danganta wannan al’amari na mace macen yara kanana da wasu tarin dalilai. Jami’in hukumar kididdiga Ouseini Lamou youssoufa ya zayyana abinda suka gano a game da wannan al’amari. A cewarsa a lokacin aka yi kiddidiga, an yi shi lokacin covid-19, lokacin al'umma ba su samu zuwa wurin likita ba, don haka yawanci yara ba su samu rugakafin ba. Yanzu haka suna so su bincika dalilin da su ka sa yara ke mutuwa kafin su kai shakara guda.

A wani abinda ke zama ci gaba a yunkurin fadakar da jama’a rashin dacewar aurar da ‘yan matan da ba su kosa ba bincike ya gano raguwar wannan dabi’a da masana suka ayyana a sahun wadanda ke barazana ga rayuwar yaran da aka yiwa auren wuri.

Sauarari cikakken rahoton cikin sauti :

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:58 0:00

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG