Daga cikin matakin da Ministan birnin Accra ya dauka na tsaftace babban birnin ghana shi ne korar masu gudanar da sana’ar su bakin titi, Inda yace Jami’an tsaro zasu kama masu Sana’a bakin titi kuma su hukuntasu.
Ministan Yankin Accra, babban birnin Ghana Henry Quarty ya bukaci duk masu gudanar da sana’o’insu a bakin titi da su tashi ko kuma hukuma da kamasu kuma ta hukuntasu.
Masu sana’ar a bakin titin birnin Accra a Ghana sun roki Ministan da ya nema musu sabon wuri kafin ya kori su daga hanyar titin.
Wata kungiyar matasa da ta fara aiwatar da aiikn korar masu sana’a a babban hanyar titin Nima daga birnin Accra ta goyi bayan kudirin ministan yankin Accra.
Quartey ya ce sun hada kai da sojojin Ghana, kuma sun horas da mazaje kusan 1,000 da za su kama duk wadana suke sana’ar a bakin titi bisa tsarin doka a wani mataki tsaftace muhalli a fadin yankin Accra.
Hukumomin Ghana Sun Haramta Cin Kasuwa A Bakin Titunan Birnin Accra

Masu sana’ar a bakin titin birnin Accra a Ghana sun roki Ministan da ya nema musu sabon wuri kafin ya kori su daga hanyar titin.
Accra, Ghana —
Labarai masu alaka
Sojojin Najeriya sun samu nasarar kwace bindigogi sama da 500
Yadda Rikicin ‘Yan Aware A Yankin Kamaru Ya Shafi Wasu Al’ummoni A Najeriya
Za ku iya son wannan ma
-
Mayu 19, 2022
Kasar Togo Ta Bude Kan Iyakarta Da Ghana
Dubi ra’ayoyi
Ko ka yi rijista da mu? Shiga shafinka
Ba ka yi rijista da mu ba? Yi rijista
Load more comments