Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Iran Ta Ce Akwai Yiwuwar Ta Tattauna Da Amurka


Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran, Abbas Mousavi
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran, Abbas Mousavi

Mousavi ya fadawa taron manema labarai da aka yada shi kai-tsaye a gidan talabijin na Press TV cewa, tattaunawar da kuma zaman sulhun zai yi wu ne idan aka tsara batutuwan da za a tattauna akai a kuma samu sakamakon mai kyau.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Abbas Mousavi, ya fada yau Litinin cewa, akwai yiwuwar a tattauna tsakanin Iran da Amurka idan har za a mayar da hankali kan ajandar da za ta kai ga samar da sakamako mai kyau, amma a cewar Mousavi, Washington ba ta neman a tattauna.

A baya, Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce a shirye yake ya tattauna tare da Jamhuriyar kasar Musulincin ta Iran.

Mousavi ya fadawa taron manema labarai da aka yada shi kai-tsaye a gidan talabijin na Press TV cewa, tattaunawar da kuma zaman sulhun zai yi wu ne idan aka tsara batutuwan da za a tattauna akai a kuma samu sakamakon mai kyau.

Amma a cewar kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran, “ba a shirye suke a tattauna ba, kuma ba sa neman a yi hakan.”

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG