Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

IRAQI: Gidan Da Aka Ajiye Akwatunan Zaben 'Yan Majalisa Ya Kama Da Wuta


 Moqtada al-Sadr shugaban Shiya wanda jam'iyyarsa ta samu rinjaye a zaben 'yan majalisar kasar Iraq da aka gudanar watan jiya
Moqtada al-Sadr shugaban Shiya wanda jam'iyyarsa ta samu rinjaye a zaben 'yan majalisar kasar Iraq da aka gudanar watan jiya

Gobara ta tashi a gidan da aka ajiye akwatunan kuri'un da aka jefa lokacin zaben 'yan majalisar kasar Iraq wadda ma'aikatan kashe gobara suka shawo kanta amma duk da haka ana kira a sake zaben

Wani gidan da aka adana akwatunan kuri’un da aka jefa a zaben ‘yan majalisar dokokin kasar Iraqi da aka yi, ya kama da wuta a jiya Lahadi, lamarin da ya sa jama’a suka fara kiran da a sake yin zaben.

Ma’aikatan kashe gobara sun garzaya zuwa wurin, inda suka yi nasarar kashe gobarar a daya daga cikin gine-gine hudu da ke dauke da akwatunan kuri’un da kuma kayayyakin zabe.

Jami’ia sun ce, zai yi wuya a ce gobarar ta shafi akwatunan, sannan suka ce, gobarar ba za ta shafi umurnin da majalisar dokoki ta bayar na a sake kidaya kuri’un ba.

Ya zuwa yanzu, ba a bayyana musabbabin wannan gobara ba, amma Kakakin majalisar dokokin kasar ta Iraqi mai barin-gado Salim Al Jabouri, ya ce da gangan aka saka wutar.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG