Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Isowar Likitocin China Zuwa Najeriya Ta Janyo Ce-Ce Ku-Ce


Wata tawagar likitocin China a kasar Serbia
Wata tawagar likitocin China a kasar Serbia

A cikin makon nan ne likitoci 15 daga kasar China da suka hada da masana da kuma kwararru masu kula da majinyata suka sauka a Najeriya, da nufin bada gudunmawa don yaki da cutar Coronavirus a kasar.

Sai dai kungiyar likitocin Najeriya NMA ta nuna rashin gamsuwa da wannan tsari, tana mai nuna tamkar hakan zai kawo koma baya ne ga lamuran harkokin kiwon lafiya a Najeriya.

Shugaban kungiyar likitoci na Najeriya, Dr. Francis Faduyile ya ce, a halin da ake ciki yanzu Najeriya na taka rawar gani a yaki da cutar ta Coronavirus, saboda haka idan ma da bukatar taimakon kasar China, za ta iya taimaka wa ta fannin kimiya da fasaha ba tare da zuwan likitocin ta Najeriya ba.

Ita ma kungiyar kwadago ta TUC, ta bakin kakakin kungiyar Nuhu Toro, ta nuna kin amince wa da gayyato likitocin, yana mai cewa “ita kanta kasar China ba ta fita daga annobar ba.”

Ya kara da cewa, Najeriya na da kwararrun likitocin da zasu shawo kan wannan annoba idan suka samu gudunmawar da ta dace daga gwamnati.

A halin da ake ciki dai yanzu, hukumar yaki da yaduwar cututtuka ta NCDC da kuma likitocin Najeriya suna aiki ba dare ba rana wajen kula da masu dauke da cutar da kuma gwajin wadanda ake zargin suna dauke da ita tare da wayar da kan jama'a kan hanyoyin da zasu bi wajen hana yaduwar cutar ta Covid-19.

Saurari wannan rahoton a sauti.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:25 0:00


Facebook Forum

Melinda Gates

BIDIYO: COVID-19 VOA Ta Yi Hira Da Melinda Gates Kan Dalilin Da Yasa Suke Taimakawa Afirka
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:08 0:00
Karin bayani akan Bidiyo
XS
SM
MD
LG