Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Isra'ila Ta Rufe Wasu Kamfanonin Dillancin Labaran Falasdinawa


Dakarun Isra'ila sun ce Falasdinawan dake neman tada zaune tsaye aka auna a samamen da aka kai.

Dakarun Isra’ila sun kai wasu samame a kamfanonin dillancin labaran Falasdinawa a yammacin kogin Jordan a cikin daren jiya, a wani farmaki da sojojin suka ce na maida murtani ne gameda tunzara mutane su yi tashin hankali akan Isra’ilawa.

Hukumomin Isra'ila sun bada umurnin rufe kamfanonin yada labarai guda 8 har na tsawon watanni shida, an kuma kama mutane biyu.

Falasdinawa sun yi Allah Wadai da samamen da Isra’ila ta kai, sun kuma ce hakan ya sabawa ‘yancin ‘yan jarida.

Wannan matakin da Isra’ila ta dauka ya zo ne ‘yan sa’o’i bayan da gwamnatin kasar ta sanar da cewa ba zata gana da gwamnatin Falasdinawa da ta hada da Hamas ba, kungiyar ta'addanci wacce take kiran a wargaza Isra'ila," kamar yadda wata sanarwa daga ofishin Firayin Ministan kasar Benjamin Netanyahu a jiya Talata ta fada.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG