Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jama'a Su Tunkari Zabe Cikin Lumana-Gargadi daga Kungiyar IZALA


Shugaban kungiyar Izalatul Bidi'a Wa Iqamatis Sunnah ta Najeriya, Sheikh Abdullahi Bala Lau
Shugaban kungiyar Izalatul Bidi'a Wa Iqamatis Sunnah ta Najeriya, Sheikh Abdullahi Bala Lau

Kungiyar izala tace bata da jam'iyya amma 'ya'yanta zasu jefawa duk wani mutumin kirki kuri'arsu

Shugaban majalisar malamai na kungiyar reshen Abuja Sheikh Ibrahim Duguri shi ya bayyana hakan a wa'azin kasa da aka yi a Abuja karshen mako.

Shugaban majalisar malamai na kungiyar Sheikh Sani Yahaya Jingir yayi kira a tunkari zaben cikin lumana. Yace addinin musulunci rayuwa ce gaba daya ciki kuma har da siyasa. Kowa ya je yayi zaben domin Allah ba domin kwadayin abun duniya ba. Su lura da cancanta da yadda za'a maido da tsaro kasar da cigaban bunkasar ilimi da tattalin arziki. Yace duk wadannan ba zasu yiwu ba sai an lura da cancanta. Duk wani dan siyasa kuma da ya fito a duba tarihinsa. Kada a yi wasa da kuri'a.

Ya yabawa INEC da tace ta shirya ta gudanar da zaben domin a wanan karon adadin wanda suka yi ragista sun fi wadanda suka yi zabe a shekarar 2011.

Kungiyar ta kira kada kowa ya bari a zolayeshi yayi fada. Gyara a ke bukata ba fada ba.

Ga rahoton Nasiru Adamu El-Hikaya domin karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:48 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG