Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jam'iyyar PDP Ta Lashe Zaben Gwamnan Jihar Ekiti


Burkina Faso Coup
Burkina Faso Coup

Zaben kujerar gwamnan jihar Ekiti da ya gudana ranar Asabar da ta gabata ya kawar da jam'iyyar APC daga mulkin jihar ya dora dan jam'iyyar PDP.

Dan takaran gwamna a tutar jam'iyyar PDP Ayo Fayose ya lashe zaben gwamnan jihar Ekiti da kuri'u dubu dari biyu da dubu uku da tasa'in. Ya kada gwamna mai ci yanzu na jam'iyyar APC Dr. Ayo Fayemi wanda ya sami kuri'u dubu dari da ashirin da hudu da talatin da uku.

Da misalin kafe daya na safiyar Lahadi Farfasa Isaac Isuzu jami'in zaben ya bayyana a ofishin hukumar zabe ta INEC dake Ado Ekiti inda ya bayyana sakamakon zaben.

Bayan da aka bayyana Ayo Fayose a matsayin wanda ya ci zaben sai magoya bayan PDP suka fantsama akan tituna suna murna.

'Yan takara goma sha takwas suka fafata a zaben da Ayo Fayose ya lashe. Mr. Banjo Oni yace a gaskiya hukumar zabe tayi adalci kuma tayi aiki mai kyau. Wani da yayi magana yace rawar da Ayo Fayose ya taka a wancan lokacin da yayi gwamna yasa mutane suka fito suka sake zabarsa.

Ga rahoton Hassan Umaru Tambuwal.
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:18 0:00
Shiga Kai Tsaye

Labarai masu alaka

XS
SM
MD
LG