Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasar Iran Na Kiyaye Sharrudan Yarjejeniyar Shirin Nukiyarta -MDD


Shugaban Iaran da shugabannin hukumar dake sa ido kan yaduwar makaman nukiliya
Shugaban Iaran da shugabannin hukumar dake sa ido kan yaduwar makaman nukiliya

Jiya Lahadi Shugaban Hukumar Hana Yaduwar makaman Nukiliya na MDD, ya ce kasar Iran na sauke nauyin da ya rataya a wuyanta kamar yadda aka tanada a yarjajjeniyar nukiliyar da ta cimma da manyan kasashen duniya.

“Zuwa yau dinnan, zan iya tabbatar da cewa Iran na kiyaye alkawarin da ta yi game da batun nukiliya a karkashin yarjajjeniyar nukiliya,” a cewar Yukiya Amano, Shugaban hukumar ta hana yaduwar makaman nukiliya, a wani taron manema labarai da aka yada a gidan talabijin na gwamnatin kasar.

Wannan sanarwar ta zo a daidai lokacin da ake takaddama tsakanin Amurka da Iran, sanadiyyar kin tabbatarwa da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi a wannan watan cewa Iran na mutunta yarjajjeniyar nukiliyar da ta cimma da manyan kasashen duniya.

Yanzu dai Majalisar Dokokin Amurka na da wa’adin kwanaki 60 na yanke shawarar ko za ta maido da takunkumin da aka kakaba ma Iran a baya wadanda aka dage mata a madadin daina shirinta na nukiliya ko a’a.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG