Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasar Turkiya Ta Gurfanar da Wasu Janar-janar 26 Gaban Kotu


 Kwamandan Mayakan Sama Janar Akin Ozturk, na cikin wadanda aka gurfanar gaban kotu da ake zarginsu da yunkurin kifar da gwamnantin kasar bara
Kwamandan Mayakan Sama Janar Akin Ozturk, na cikin wadanda aka gurfanar gaban kotu da ake zarginsu da yunkurin kifar da gwamnantin kasar bara

A kasar Turkiya, an soma shara’ar mutane 220 da suka hada da manyan hafsoshin soja 26 masu mukaman janar-janar, wadanda ake zargi da taka rawa a yunkurin juyin mulkin da aka so yi a watan Yulin shekarar da ta gabata.

Daga cikin wadanda aka gurfanar a gaban kotu harda General Akin Ozturk, tsohon babban kwamandan mayakan jiragen sama na kasar.

Turkiya dai tana zargin wani hamshakin malami dan kasar Turkiya dake zaune a nan Amurka mai suna Fethullah Gulen da laifin kitrsa makircin yunkurin juyin mulkin na ran 15 ga watan Yulin 2016, wanda mutane fiyeda 260 suka rasa rayukkansu a cikinsa.

Gulen dai ya musanta zargin cewa yana da hannu cikin lamarin.

A jiya Lahadi ne kuma shugaban Turkiyar, Recep Tayyip Erdogan ya kara tsawaita dokar ta-bacin da aka kafa tun bayan yunkurin juyin mulkin na bara.

A karkashin wannan dokar-ta-bacin ne aka kame mutane fiyeda 47,000, sannan an kori wasu 100,000 daga aiyukkansu a bisa tuhumar cewa sun taka rawa cikin yunkurin.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG