Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasashen Tarayar Turai Za Su Kafa Rudunar Kula Da Kan Iyakoki


Wasu bakin haure
Wasu bakin haure

A cigaba da neman bakin zaren game da yawan shiga Turai da bakin haure ke yi, kasashen Turai za ku kafa wata runduna ta kula da zirga-zirgar jama'a a kan iyakoki musamman na wasu kasashe.

Wadansu kasashe ne na Tarayar Turai da su ka hada da kasar Jamus da kasar Hommand za su tallafa wa wadansu takwarorin su na Nahiyar Africa Nijer na daga cikin su, wannan ko domin girka wata runduna mai kula da iyakokin su don hana kwararar bakin haure da ke neman ko a mutu ko ayi rai sai sun Shiga kasashen turai.…….

Dama shugaban kasar Nijer Alhadji Issuhu Mahamadu, a taron kasashe masu anfani a bai daya da halshen Faransanci da ya wakana a kasar Armeniya, ya nuna muhimmancin kasancewa tare a wannan yakin.

Sai dai, yanzu haka, wadansu magabata a jahar Agadez, da ke kasancewa matattarar bakin haure masu neman zuwa Turai na ganin dokar da kasar ta dauka domin takawa masu safarar bakin haure da ma bil'adama burki na da sauran rina a kaba.

Ga wakiliyarmu Tamar Abari da cikakken rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:38 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG