Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kawo Yanzu Rikicin Afirka Ta Tsakiya Ya Hallaka Mutane Fiye Da Dubu


Wani rikici
Wani rikici

Shugabannin wasu kasashen afirka zasu yi taro yau alhamis domin tattauna Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, inda aka kashe mutane fiye da dubu daya a fadan da ake yi tun watan Disamba.
Kungiyar Kasuwar tattalin Arzikin Tsakiyar Afirka, ECCAS, ita ce ta shirya wannan taron da za a yi a Chadi makwabciyar Jamhuriyar.
Ministan yada labarai na jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, Adrien Poussou, ya fadawa Muryar Amurka cewa shugaba Michel Djotodia, shi ne ya bukaci da a yi wannan taron domin tattauna yadda za a mayarda rundunar sojojin kasashen Afirka zuwa ta aikin kiyaye zaman lafiya ta MDD a Jamhuriyar.
Yace shugaban rikon kwaryar zai kuma bayyanawa shugabannin kasashen yankin irin halin tsaron da ake ciki a Bangui, babban birnin kasar.
Poussou yace babu gaskiya a cikin rahotannin da ma’aikatar harkokin wajen Faransa ta bayar cewa mahalarta taron zasu tattauna a kan ko ya kamata Mr. Djotodia ya ci gaba da kasancewa a kan karagar mulki.
Mr. Djotodia ya karbi ragamar ikon kasar a bayan da ‘yan tawayen kungiyar Seleka wadda Musulmi suka fi yawa a ciki, suka hambarar da shugaba Francois Bozize a watan Maris na bara. Tun daga lokacin, Jamhuriyar Afirka ta tsakiya ta tsunduma cikin fitina, akasarinta a tsakanin tsoffin ‘yan tawayen Seleka da kungiyoyin sojojin sa kai na mabiya addinin Kirista.
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG