Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kira Ga Mata Kukama Sana'a Don Dogaro Da Kai

Wasu mata masu na'a
Wasu mata masu na'a

Wata baiwar Allah mai dogaro da kanta batare da ta jira mijinta ba

Wata baiwar Allah Malama Hadiza Yusuf tace bata yarda ta zauna ba a ce komai sai mijinta yayi mata don wannan raguwar dubara ce. Ta kasance tana sana’o’I kamar kala hudu, kuma tana da ‘yaya uku kuma tana ganin ala dole mata su tashi su nemi na kansu kada suce sai abun da maigida yabada sannan za’ayi amfani da shi.

Wadannan sana’o’in na ta basu sa tazama wadda bazata iya aiwatar da duk wani abu da yakamata tayi a matsayinta na matar aure ba. Wannan ma wani karfin gwiwa yake bata. Sai dai tayi nuni da cewar matsalolin da suke samu shine ana karban kayan bashi kuma ba’a biya kan lokaci.

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:39 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

XS
SM
MD
LG