Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kiran Dage Zaben Dake Tafe Bada Yawunmu ba

PDP
PDP

Yanzu haka,al’ummomin da hare-haren yan Boko Haram ya raba da gidajen su da sauran masu ruwa da tsaki, sun fara maida martani ga kalaman da gwamnan jihar Adamawa, Mr Bala James Ngillari yayi a wani taro na masu ruwa da tsaki da hukumar zabe ta yi da hukumomin jihohin Adamawa, Borno da Yobe, inda gwamnan Adamawan yayi kira da a dage zaben dake tafe a watan gobe, har zuwa watan Afrilu.

Alhaji Umaru Duhu , dan takara ne a inuwar jam’iyyar APC, a yankin Madagali, yace sun yi mamakin wannan kiran da gwamnan yayi na a dage zabe, ya kara da cewa bada yawunsu yayi ba.

Shi dai gwamnan Adamawan, wanda yanzu haka mahaifarsa ta Madagali ke hannun mayakan Boko Haram, na cikin yan takara a zaben dake tafe, inda jam’iyarsa ta PDP, ta bashi tikitin tsayawa takarar kujerar majalisar dattawa.

Dage zabe - 3'08"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:08 0:00

XS
SM
MD
LG