Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotu A Jihar Neja Ta Mika Ikon Garin Piyame Ga Kabula Fada


Kotun koli ta yanke hukuncin mika garin Piyame ga wani attajiri mai suna Kabulu Fada bayan an jima ana tafka sharaa game da mallakar wannan garin.

Mutanen garin Piyame dake cikin karamar hukumar shiroro sun shiga tsaka mai wuya, sakamakion hukuncin da babban kotu ta yanke game garin na Piyame.

Yanzu haka dai kotun koli ta yanke hukuncin cewa garin na Piyame ya koma mallakin wani mutum da ake kira Kabulu Fada.

An kwashe shekaru da dama ana tafka sharaa game da mallakar wannan gari tsakanin wannan attajirin da mutanen garin wanda suke ikirarin cewa iyayen sune suka kafa garin

A cikin wannan satin ne kotu ta yanke hukuncin mika garin ga wannan mutumin.Abinda gwamnan jihar Alhaji Abubukar Sani Bello ya shigo cikin maganar domin gudun tashin hankali.

Ga Mustafa Nasir Batsarida Karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:35 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG