Wadanda aka gurfanar din sun hada da tsohon kwamishinan kudi, da tsohon shugaban jamiyyar PDP, da kuma tsohon jami’in zirga-zirga na harkokin gidan gwamnati a wancan lokacin.
Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa ce wato EFCC, ta gurfanad da mutanen.
Ana dai tuhumar su da satar wasu kudi daga cikn kudaden da aka ware domin sayen kayan abinci na ‘yan gudun hijira.
Kudin da suka kai sama da naira miliyan dari biyar sunyi batan dabo ne sai’ilin sayen kayayyakin abincin ‘yan gudun hijira.
Ga Ibrahim AbdulAzeez da karin bayani.
Facebook Forum