Wasu shugabannin wata kungiyar mayaka masu tsattsauran ra’ayi ta Pakistan su 4, da ke da alaka da wasu munanan hare-hare da aka kai a makwabciyar kasar India, an tabbatar sun aikata laifin samar da kudaden ayyukan ta’addanci.
Wata kotu ta musamman da ke gabashin birnin Lahore ce ta yanke hukuncin a ranar Alhamis wanda ya gano cewa lallai mutanen su hudu sun aikata laifin tara kudade da kuma samar da kudade ba bisa ka’ida ba don ayyukan kungiyar Lashkar-e-Taiba, wadda kuma ake kira kungiyar LeT.
An haramta kungiyar ta LeT a Pakistan tun a shekarar 2002.
Jami'an Indiya da na Amurka sun zargi kungiyar da kitsa hare-haren ta'addancin da aka kai a Mumbai wanda suka yi sanadiyar kisan mutane 166 a shekarar 2008.
Ma’aikatar yaki da ta'addanci ta lardin Punjab, wadda ta gudanar da bincike tare da gabatar da kara, ta bayyana sunayen mutanen, Zafar Iqbal, Yahya Aziz, Abdul Rehman Makki da Abdus Salam.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum